Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Farfesa Sani Abubakar Lugga, Wazirin Katsina na 5, ya yi kira ga yankin Arewa da su haɗa kai su shirya don cin gashin kansu, kamar takwarorinsu na Kudu.
Da yake jawabi a wajen taron wayar da kan al’umma da ƙungiyar haɗin kan Arewa CNG ta shirya a Katsina, Lugga ya jaddada buƙatar ‘yan Arewa su jajirce wajen yiyuwar ɓallewa daga Nijeriya, tare da yin la’akari da kiraye-kirayen ɓallewa daga Kudu.
Lugga ya koka da rashin haɗin kai a tsakanin ‘yan Arewa wajen kare ‘yancinsu, inda ya kwatanta hakan da yadda ƙungiyoyi irin su ‘yan Biyafara suke yi.
Ya buƙaci Arewa da ta yi koyi da irin matakan da jihohin Kudu ke ɗauka, musamman wajen magance matsalolin tsaro. Ya yi nuni da cewa, duk da cewa al’amuran tsaro ba su da yawa a Kudancin ƙasar, sun kafa jami’an tsaro a yankin kamar Amotekun, yayin da Arewa ta ci gaba da zama ba ruwanta.
Da yake tsokaci kan abubuwan da suka shafi tarihi, Lugga ya bayyana fargabar shugabannin Nijeriya na farko game da haɗewar Arewa da Kudu, ƙungiyar da a cewarsa har yanzu tana da rauni. Ya yi gargaɗin cewa idan ba a shirya ba, Arewa za ta iya yin gwagwarmayar rayuwa idan Kudu ta yi nasarar ɓallewa.
Jami’in CNG na ƙasa Jamilu Charanchi, ya kuma jaddada gaggawar ayyukan da al’umma ke jagoranta don magance matsalolin tattalin arziki da tsaro na Nijeriya. Ya soki shugabannin ƙasar kan yadda suka fifita zaɓe fiye da makomar al’umma sannan ya buƙaci al’umma da su ɗauki nauyin tafiyar da rayuwarsu ta hanyar haɗin gwiwa.
