Gaisuwar ‘Dobale’ na yi a ranar demokraɗiyya: Shugaba Tinubu

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya magantu kan tuntuɓe da ya yi yayin hawa motar zagaye a ranar bikin cikar demokradiyya shekaru 25 ganin yadda ɗaukar ta karaɗe shafukan sada zumunta da sauran gidajen jaridu.

A lokacin da yake magana wajen cin abincin bikin demokraɗiyya a daren Laraba a fadar shugaban ƙasa, Tinubu cikin raha yace, mutane sun gagara fahimtar rawar waƙar ‘Buga’ ce ko kuma gaisuwar al’ada ta ‘Idobale’ ce ya yi a lokacin aukuwar lamarin.

Shugaba Tinubu, ya ƙara da cewa, hakan na nuna farin cikinsa ga ranar demokradiyya da kuma girmama al’adar ƙabilarsa ta Yaroba.

By Babaji