Daga IBRAHIM HAMISU a Kano
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya umarci dukkan masarautu huɗu a jihar da su fara shirye-shiryen hawan Sallah.
Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, a wata sanarwa da ya fitar ya ce gwamnan ya bada umarnin ne yayin da ya yi buɗe-baki da Sarakuna hudu na jihar, ƙarƙashin jagorancin Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi ll a ranar Talata a fadar gwamnatin.
A cewar gwamnan, al’ummar Kano sun ƙagu lokacin Sallah ya zo su ci kwalliya su je kwallon hawa don samun nishaɗi daga al’adun jihar.
Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba za ta bari wani abu ya gindaya da zai hana mazauna jihar samun wannan dama ta bikin sallah ba.
Ya bayyana cewa akwai shiri da aka tanada ta yadda jami’an tsaro za su bada kariya da tabbatar da cewa an yi bukukuwan sallah lami lafiya a jihar ba tare da wasu ɓatagari sun kawo cikas ba.