
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Gwamnatin Tarayya ta dakatar da jami’an Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali (NCoS) guda biyu kan yunƙurin samar wa wani fursuna fasfo.
Kakakin hukumar, Umar Abubakar ya sanar da batun a wata takarda, inda ya ce wani mataimakin kwantirola ya bayyana hakan a matsayin saɓa wa dokar aikinsu.
Haka kuma ya saɓa wa wasu dokokin gyare-gyare na Hukumar Shige da Fice NIS.
Ya ce, an gano haka ne a lokacin da ake aikin haɗin-gwiwa a tsakanin hukumomi da Ma’aikatar harkokin cikin gida.
Kakakin ya kuma ce, al’amarin ya auku ne makonni biyu da suka gabata, wanda ya ci karo da dokokinsu da aka amince da su don haka sai an hukunta su bisa laifin.
Ya ƙara da cewa, hukumar tana aiki tuƙuru wajen ganin ta tabbatar da horo da tsayar da gaskiya da adalci a gidajen yarin Nijeriya.
Kazalika, ya ce hukumar ta ce duk wanda aka kama da hannu a saɓa ƙa’idar aiki ko rashawa ko zagon-ƙasa, to za a sallame shi a aiki.
