Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
A cikin shekaru biyu da suka gabata, gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar da manyan sauye-sauye a fannin fansho da suka kawo ƙarshen wasu matsalolin da suka daɗe suna addabar masu ritaya, tare da ƙara yawan kuɗaɗen da suke karɓa a kowane wata.
Darakta Janar ta Hukumar Kula da Fansho ta ƙasa (PenCom), Misis Omolola Oloworaran, ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Talata.
Ta ce gwamnatin ta kashe Naira biliyan 758 domin biyan haƙƙoƙin fansho da suka taru tun daga shekarar 2007, lamarin da ya amfani kusan mutum 957,045.
A cewarta, wannan mataki ya rage gibin biyan haƙƙoƙin fansho daga jinkirin watanni 21 zuwa yanayin da gwamnati ke da tanadin watanni 41 a gaba.
Omolola ta bayyana cewa jimillar kuɗaɗen da ke cikin tsarin fansho ta ƙaru daga Naira tiriliyan 20.79 zuwa Naira tiriliyan 31.48 cikin shekaru biyu kacal.
Ta ce hakan na nuna yadda amincewar ma’aikata da tsarin ta ƙaru, yayin da sama da sabbin ma’aikata 938,000 suka shiga tsarin fansho a wannan lokaci.
Ta ƙara da cewa gwamnati ta ƙaddamar da shirin Pension Boost 1.0, wanda ya ƙara jimillar kuɗin fansho da ake biya duk wata daga Naira biliyan 12.2 zuwa biliyan 14.9.
Hakazalika, gwamnatin ta amince da ƙarin Naira 32,000 ga dukkan masu ritayar ma’aikatun gwamnatin tarayya da suka yi ritaya kafin ranar 29 ga Yulin 2024, domin daidaita fanshonsu da sabon mafi ƙarancin albashi.
Ta kuma bayyana cewa an yi bitar fanshon tsofaffin ma’aikatan NSITF karo na farko cikin shekaru 21, inda wasu suka tashi daga karɓar Naira 18,000 zuwa Naira 206,000 a kowane wata, tare da biyansu basussukan da ake binsu.
