Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Aƙalla mutane 40 wanda akasari mata da yara ne aka ruwaito sun rasa rayukansu a qauyen Badau da ke qaramar hukumar Bagwai a jihar Kano sakamakon wani hatsarin kwale-kwale.
Wani wanda abun ya faru a gaban idonsa wanda kuma ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce, hatsarin ya faru ne a ranar Talata da misalin ƙarfe 6 na yamma.
Ya bayyana cewa, kwale-kwalen ya kife ne a tsakiyar kogin yayin da yake jigilar fasinjoji zuwa garin Bagwai daga ƙauyen Badau.
Waɗanda lamarin ya rutsa da su sun mutu ne a cikin kogin saboda ba za su iya yin iyo zuwa gaɓar kogin ba kuma ba sa sanye da rigar ceto.