Iya Alakara: Tinubu ya yi wa Oluremi ba’a yayin cece-kucen sayar da ƙosai

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Shugaba Bola Tinubu ya nishaɗantar da jama’a a wajen wani taro da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, bayan da ya kira Uwargidansa, Sanata Oluremi Tinubu da “Iya Alakara”, wato Mai ƙosai ko Mamar ƙosai.

Tinubu ya furta haka ne a wani yanayi na barƙwanci yayin da yake gabatar da manyan baƙi a wajen liyafar da aka shirya wa ‘yan jaridar fadar.

Kalaman shugaban ƙasar na zuwa ne bayan cece-kucen da suka biyo bayan shawarar da Oluremi ta ba mata da su rungumi ƙananan sana’o’i kamar su sayar da ƙosai, masara gasassa, ƙarago, tumatur, barkono da kayan lambu, inda ta ce ire-iren waɗannan sana’o’i ba sa buƙatar babban jari.

Waɗannan kalamai sun haddasa suka daga wasu ‘yan Nijeriya da suka ce ba su yi daidai ba da halin matsin tattalin arziƙin da al’ummar ƙasar.

Daga bisani Sanata Oluremi Tinubu ta fayyace cewa shirin tallafin gwamnatin tarayya ba na masu sayar da akara (ƙosai) kaɗai ba ne, saidai yana shafar dubban ƙananan ‘yan kasuwa.

Haka kuma, ta ce Gwamnatin Tarayya ta bayar da Naira miliyan 100 domin tallafa wa ƙananan ‘yan kasuwa 2,000 a Jihar Jigawa, tare da jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa sana’o’insu domin su kasance masu ɗorewa a harkokin kasuwancinsu.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da al’umma ke fuskantar halin matsin tattalin arziƙi a Nijeriya yayin da gwamnatin ƙasar ke cigaba da ƙoƙarin ganin ta shawo kan al’amarin ta hanyar sauye-sauye da kuma wasu shirye-shirye na tallafa wa masu ƙananan ƙarfi a sassan ƙasar.

By Babaji

Leave a Reply