Kotu ta umarci a yi sabon zaɓe bayan tsige ɗan Majalisar Wakilai na Zamfara kan koma wa APC

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige ɗan Majalisar Wakilai, Abubakar Gummi kan sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Ɗan majalisar shi ke wakiltar mazaɓar Gummi/Bukkuyum ta tarayya daga Jihar Zamfara.

Da yake gabatar da hukunci, Alƙali Obiora Egwuatu ya haramta wa Kakakin Majalisar Wakilan, wato Tajudeen Abbas cigaba da ɗaukar Abubakar Gummi a matsayin mamba a majalisar.

Haka kuma, Mai Shari’ar ya umarci hukumar zaɓe, INEC da ta shirya gudanar da sabon zaɓe acikin kwana 30 domin cike gurbinsa.

Jam’iyyar PDP da Shugabanta na jihar, Jamilu Jibo-Magayaƙi ne suka shigar da ƙarar bayan sun zargi ɗan majalisar da watsa musu ƙasa a ido duk da cewa PDP ce ta ɗauki nauyinsa har ya ci zaɓe a lokacin da babu rarrabuwar kai acikinta.

Haka kuma, ya ƙaƙaba tara akan wanda aka shigar ƙara na N500,000, kuɗaɗen da zai biya ɓangaren da suka shigar da shi ƙara.

By Babaji