Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Jam’iyyar NNPP ta musanta rahotannin da ke cewa jagoranta na kasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya tattauna ko yana shirin sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC.
A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Ladipo Johnson, ya fitar, ya bayyana zarge-zargen a matsayin karya da kuma wani yunkuri na wasu jiga-jigan siyasa na bata sunan Kwankwaso.
Ya ce Kwankwaso bai taba tunanin shiga APC ba, kuma bai taba ganawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ko wakilansa domin tattauna batun sauya sheƙa ba.
Johnson ya ce ganawar karshe da Kwankwaso ya yi da Tinubu ta faru ne a watan Janairun 2024, kuma ba a taba tattauna batun sauya sheƙa a lokacin ba.
Ya bayyana cewa abin takaici ne yadda ake kirkirar irin wadannan labaran karya, yana mai zargin cewa masu yada jita-jitar sauya sheƙar su ne wadanda suka yi niyyar komawa APC kuma wasu daga cikinsu sun riga sun yi hakan.
Ya kuma zargi wasu jiga-jigan siyasa da hada baki domin rage tasirin Kwankwaso ta hanyar yada labaran karya da ra’ayoyi marasa tushe a kafafen yada labarai, yana mai cewa hakan wani yunkuri ne na hana yiwuwar hadakar siyasa da ka iya kalubalantar tsarin mulkin da ake ciki.
