Macron ya sake lashe zaɓen Faransa

Shugaban Ƙasar Faransa, Emmanuel Macron ya lashe babban zaɓen ƙasar da aka gudanar inda ya doke abokiyar hamayyarsa Marine Le Pen.

Macron ya lashe zaɓen ƙasar ne wanda aka kammala a ranar Lahadi.

DW ta ruwaito cewa Mr. Macron ya samu kashi 58.2% cikin ɗari ne na ƙuri’un da aka kaɗa.

Yayin da abokiyar hamayyarsa, Marine Le Pen wadda ta amsa shan kaye, ta samu kashi 41.8% cikin ɗari.

‘Yar takarar adawar, Marine Le Pen, ta lashi takobin ci gaba da gwagwarmaya musamman ma wajen ganin ta taka rawa a zaɓen majalisar dokokin ƙasar da ke tafe.

Tuni ma shugabannin gwamnati da hukumomi da ma ‘yan siyasar nahiyar Turai suka taya Shugaba Macron murnar sake lashe zaɓen na Faransa.