Daga AMINA YUSUF ALI
Ƙungiyoyin ‘yan ƙwadago ta NLC da TUC sun nemi gwamnatin Bola Ahmad Tinubu da ta biya Naira 497,000 maimakon Naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi.
A taqaice dai ma wato sun sassauta abin da suke buƙata gwamnati ta biya a matsayin mafi ƙarancin albashi a ƙasar zuwa naira 497,000.
A baya dai ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce dage a kan Naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi da suke son gwamnatin ƙasar ta amince da shi.
Yayin cigaba da tattaunawar a ranar Talatar da ta gabata, ƙungiyoyin sun kuma yi watsi da sabon ƙudirin da gwamnati ta gabatar na naira 54,000 a matsayin albashi mafi ƙaranci.
Haka kuma a ranar Laraba kwamitin ƙarin albashin ya bai wa NLC tayin naira 57,000 a matsayin mafi ƙarancin albashin, inda nan take ƙungiyar ƙwadagon ta yi fatali da tayin. Har dai yanzu ba a cimma matsaya ba tsakaninsu.
