Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina
Tsohon sakataren hukumar zaɓe na kasa maraɗin Katsina kuma Hakimin kurfi ya rasu.
Ya rasu a babban asibitin gwamnatin tarayya da ke Katsina yana da shekara 90.
Marigayi Ahmadu kurfi ya taba riƙe sakataren hukumar zaɓe na ƙasa(FEDECO) a shekarar 1999.
Kafin nan marigayin ya fara aiki a mulkin Sardauna Ahmadu Bello a 1958 .
Ya kuma riƙe muƙamin babban sakatare a ma’aikatun gwamnatin tarayya guda uku kafin ya ajiye aiki a shekarar 1986.
Daga nan ne ya sami sarauta maraɗin Katsina Hakimin kurfi.
