NIS ta dakatar da ɗaukar hutu ga ma’aikata kan zanga-zangar tsadar rayuwa

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

La’akari da zanga-zangar tsadar rayuwa da ke tafe a watan Agusta, hukumar shige da fice, NIS ta sanar da dakatar da neman zuwa hutu ga ma’aikatanta na wucin-gadi.

Kwamturola Janar ta hukumar, Misis Kemi Nandap ta bada umarni ga shugabannin shiyyoyi da na jihohi da kuma na yankuna, inda ta ce akwai buƙatar aiki na musamman a kan iyakokin ƙasa domin tabbatar da tsaro a lokacin zanga-zangar.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Kenneth Udo ya fitar, hukumar ta ce tana shirye-shirye domin tsare duk wani kutse da ka iya tunkaro ƙasar daga waje da zai yamutsa al’amari.

Zanga-zangar tsadar rayuwa a Nijeriya ya biyo bayan wacce ƴan ƙasar Kenya su ka yi a makonnin da su ka gabata kan hauhawar kuɗin haraji wanda hakan ya tilasta wa shugaban ƙasar sauya matsayarsa.

An shirya zanga-zangar ne musamman ta kafofin yaɗa labarai na zamani kamar yadda ya ke faruwa a Nijeriya.

By Babaji