Ogun: ‘Yan bindiga sun sace Sarkin Ijebu-Igbo

Daga WAKILINMU

Rahotanni daga yankin Ijebu-Igbo a jihar Ogun sun nuna wasu ‘yan bindiga sun sace sarkin yankin, Oba Alade Meta, a ranar Asabar.

Wata majiya ta ce a wannan rana, sarkin ya bar fadarsa da misalin ƙarfe 11 da wata motarsa ‘jeep’ zuwa unguwa. A kan hanyarsa ta komawa gida misalin ƙarfe 3 na rana, ‘yan bindiga suka tare shi a hanya, suka fidda shi a motarsa tare da yin awon gaba da shi sanna suka bar motar tasa a nan.

Tun daga wannan lokaci ya zuwa haɗa wannan labari, babu wanda ya san inda sarkin yake. Haka ma ‘yan sandan yankin ba su kai ga tabbatar da faruwar lamarin ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *