Rubutun Turanci ya fi min sauƙin rubutawa da sarrafa jigo – Fatima AbbaGana

Spread the love

“Ina ba littafi daraja sosai fiye da yadda a ke zato”

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU 

Sunan Fatima Ibrahim AbbaGana ba ɓoyayye ba ne a tsakanin marubutan adabi na Nijeriya, musamman saboda yadda take da zumunci da ilimin zama da jama’a. Bayan kasancewarta marubuciya, Fatima ta kasance tsohuwar ma’aikaciyar banki, ýar kasuwa, kuma ƙwararriya kan binciken shigi-da-ficen kuɗi. Ta rubuta littattafai daban-daban cikin harshen Hausa da Turanci, inda take mayar da hankali kan labaran da suka shafi raya al’ada, inda zamantakewa da kyautata tarbiyya. Ita ce ta rubuta littafi mafi girma da wata marubuciya a Arewa ta wallafa, domin kuwa littafin ta na Bunayya an raba shi har kashi huɗu kuma kowanne ɓangare na ɗauke ne da labari mai kama zuciya da riƙe mai karatu. Fatima Abba Gana, mamba ce a ƙungiyoyin marubuta daban-daban na duniya.

MANHAJA: Ki gabatar mana da kanki.

FATIMA ABBA GANA: Sunana Fatima Ibrahim Abba Gana. Tsohuwar ma’aikaciyar banki. Marubuciyar littattafan Hausa da Turanci, manazarciya, mai fassarar Turanci da Hausa, kuma mai taimakon al’umma. ‘Yar kasuwa, shugabar kamfanin Shawullam Nig LTD dake gudanar da ayyukan kwangila da kasuwanci.

Za mu so mu ji tarihin rayuwarki.     

Ni, Fatima Ibrahim Abba Gana haifaffiyar garin Kaduna ce, kuma na yi rayuwata a garuruwan Arewa daban-daban. Asalina mutuniyar Jihar Barno ce daga ƙabilar Kanuri. Na yi karatun boko da na addini har zuwa matakin Digiri, inda na samu digirin farko a Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya. Na yi aikin Hidimar ƙasa a garin Osogbo na Jihar Osun, na samu damar aiki a ofishin Gwamnan jihar.

Na yi aiki a matsayin Akawu a kamfanin Paki International Motors a Kaduna, kafin daga bisani na koma aikin banki tare da Bank PHB. Na kuma yi aiki da Union Bank har na kai matsayin Manaja, sannan na yi aiki na wani lokaci a Ja’iz Bank. Bayan na bar aikin banki da kimanin shekaru goma sha biyar sai na buɗe nawa kamfanin na kaina.

Na yi kwasa-kwasai da dama a fannin aikin banki da kuma abinda na karanta har da babbar jarrabawar nan ta ƙwararrun masu aikin Akawu wato ACCA dake Ingila. Na kuma halarci shahararriyar makarantar nan ta Legas wanda aka fi sani da Goethe Institute, inda na samu shaidar Difloma ta jin harshen Jamusanci. Na kuma yi babbar makarantar da ake horar da masu aikin shirya finafinai dake Legas wato ITPAN ( Independent Television Producers Association of Nigeria), inda na samu kwalin shaidar ƙwarewa a fannin rubuta labarin fim, shiryawa da kuma ba da umarni.

Yanzu haka ni ce shugabar kamfanin Shawullam Nig. LTD wanda yake ayyukan kwangila, da kuma aikin binciken shigi-da-ficen kuɗaɗe. Muna kuma da sashin dake kula da abin da ya shafi harkokin raya adabi da al’adu da rubuce-rubuce, a gefe guda. Ina da son yawan tafiye-tafiye, nazarce-nazarce da rubuce- rubuce. Ina kuma da sha’awa kan hidimar aikin taimakawa al’umma.  Yanzu haka ni mamba ce a ƙungiyoyin marubuta da dama, kamar Soceity of Young Nigerian Authors (SYNW), International Women Writers Guilld (IWWG USA), ƙungiyar LITACO dake Legas da kuma ƙungiyar marubutan Nijeriya ta ANA reshen Abuja. Yanzu haka kuma ni ce  Mataimakiyar Shugaban ƙungiyar marubutan Jihar Kaduna ta Alƙalam.

Ba mu labarin yadda aka yi ki ka zama marubuciya.

Tun ina ƙarama na taso da sha’awar karance-karance, har ina fatan nima watarana na rubuta littafi na kaina. Ba na mantawa lokacin ina firamare na yi ta ýan rubuce-rubuce ƙanana ina adanawa. Sannan ina da son yawan karance-karancen littattafan Turanci da na Hausa. Har zuwa lokacin da na girma na shiga aikin banki na cigaba da rubuce-rubuce kuma sannu a hankali har na samu kaina a cikin harkar sosai. Rubuce-rubucena sun kasance na daban, saboda irin saƙonnin da nake isarwa da salon rubutuna da nake yi cikin harsuna biyu, inda nake taɓo batutuwan da suka shafi ƙalubalen da mata da cigaban al’adun mutanen Afirka da zamantakewar  al’umma.

Tsakanin marubuciya da makaranciya wanne ki ka fara zama?

Na fara da zama makaranciyar na littattafai daban-daban daga na Hausa zuwa Turanci da wasu harsunan daban. Sannan daga baya nima na zama marubuciya, ina rubuta labarai da hikayoyi masu jan hankalin mai karatu. Ina da littattafai da nake tarawa a ɗakin karatuna da yawansu ya kai fiye da dubu biyar. Kuma har yanzu ban daina sayen littafi ba, in dai an ce wannan littafi ne mai amfani to, za ka samu ina da shi ajiye. Kuma a gaskiya ina ba littafi daraja sosai fiye da yadda ka ke zato, domin ko kyautar littafi aka bani yana da daraja a wajena kwarai da gaske.

Na karanta littattafai da dama da ba zan iya zayyano su duka ba, kaɗan daga cikin marubutan da na karanta littattafansu, akwai su irin su John Grisham, Barbara Taylor Bradford, Sidney Sheldon, Robert Ludlum da Mario Puzo cikin marubutan yammacin duniya. Amma a cikin marubutan Hausa da na Afirka akwai marubuta irin su Hajiya Balaraba Ramat Yakubu, Farfesa Zaynab Alƙali, Farfesa Razinat Muhammed, Bala Anas Babinlata, Dan’azumi Baba Cediyar ‘Yan Gurasa, Nazir Adam Salihi, Balkisu Ahmed Funtua, Chinua Achebe, Farfesa Wole Soyinka, Ngugi Wa Thiong’o da sauran su da dama.

Akwai wani wanda ya fara koya miki yadda ya dace ki tsara labarinki ko ya koya miki ƙa’idojin rubutun Hausa?

Gaskiya babu wanda ya koya min, sha’awa ce kawai da yawan karatuna ya jefa ni cikin aikin Akawu har na zama mai aikin banki, kafin in zama cikakkiyar marubuciya. Kuma burina nima in bar wa na baya abin koyi ko ba na raye a cikin ayyukana na harkar rubutun adabi.

Kawo yanzu kin rubuta littattafai guda nawa?

Alhamdulillahi. Na rubuta littattafai aƙalla bakwai, cikin har da na Hausa da na Turanci, wasu kuma za ka samu littafi ne guda ɗaya amma yana da kashi-kashi. Daga cikin littattafan da na wallafa akwai ‘Raƙiba’ na Hausa da Turanci, akwai littafin ‘Karima’ na Hausa, sai kuma littafin ‘Bunayya’ na turanci mai kashi hudu. Na farko na sa masa suna Bunayya, The Zaria Impact, sai Bunayya, The Fire Beneath, da Bunayya, The Broken Kola, sai Bunayya, The Lost Soul The Last Rite.

Sauran littattafan sun haɗa da ‘The Deceptive Heart’ shi ma na Turanci ne, sai wani na Turancin, ‘Whispers in the Heart’. Ina kuma da ‘Kukan Ruhi’. littafin Hausa, da ‘Tsarki A Cikin Guba’, shi ma na Hausa ne, sai ‘Rijiyar Sirri’. Ina kuma da Gajerun Labarai irin su ‘Garin Da Barci’, ‘Sakaci’, da ‘Nahawun Yunwa’.

Sannan kuma na yi aikin fassarar wasu littattafai daga Hausa zuwa Turanci. Sun haɗa da littafin ‘For the Sake of Love’ wanda fassara ne daga littafin ‘A Dalilin So’ na Badamasi Su’aibu Burji, sai kuma littafin ‘When Love Reaches its Peak Money Has No Influence’ wanda shi ma fassara ne daga littafin ‘Idan So Ya Yi So’, shi ma Badamasi Shuaibi Burji ne ya rubuta. Na kuma fassara littafin Hafsat S. Mohammed daga ‘Soyayyar Da Ba Ta Da Shinge’ zuwa ‘Love Has No Boundary’. 

Tsakanin rubutun Turanci da na Hausa wanne ya fi miki sauƙin rubutawa da sauƙin sarrafa jigo?

Rubutun Turanci ya fi min sauƙin rubutawa da sauƙin sarrafa jigo.

Me ya ja ra’ayinki ga rubutun littafin Bunayya? Me ya sa ki ka raba shi har gida 4?

Ana yawan min tambaya akan littafin Bunayya, kasancewarsa guda huɗu kuma labari ɗaya ne. Mafi yawan lokaci sai dai in yi murmushi, sannan in bada amsa. Labarin Bunayya an raba shi huɗu ne domin kowanne littafi yana ƙunshe ne da labari na daban mai zaman kansa, wanda idan aka haɗe shi zai iya zama labari guda. Na yi wa labarin tsarin da kowanne ɓangare yana nuna muhimmancin riƙo da gargajiya, al’adu, dabi’un mu, da muryar al’ummar Arewacin Nijeriya.

Ba mu taƙaitaccen bayani game da labarin da littafin Bunayya ya ƙunsa.

Littafin Bunayya yana ɗauke ne da labarin wata ‘yar jarida ce da take aiki kan wani rahoto mai cike da sarƙaƙiya da abubuwan ban al’ajabi da  ban mamaki. Binciken da take yi ya kai ta har zuwa wani da ake kira da Zariya, inda a nan ne ta ci karo da wasu abubuwa na tarihi da suka haɗa da wasu tsofaffin rubuce-rubuce na ajami, wanta ta tsinta a cikin wata ƙwarya. Wannan shi ne ya zama tushen fara labarin da ƙalubalen da ta shiga, da irin matsalolin da ta yi ta cin karo da su, waɗanda suka riƙa sa rayuwarta a cikin hatsari. Lokacin da sirruka suka bayyana, aminci da yarda suka yi rauni, Bunayya ta shiga wami ƙalubalen zaɓi biyu, tsakanin soyayya da gaskiya, ba tare da ta san wannan abin da ta samu shi ne zai zama mata ƙalubale da tirka–tirka a rayuwarta ba.

A kashi na biyu na littafin Bunayya, The Fire Beneath, ya taɓo yadda binciken Bunayya ya kai ta Birnin Kano. A nan ma ta gamu da,wasu abubuwan na al’ajabi da suka zama shaidar yaudara da cin amana, wanda ya taɓa rayuwar ta bakiɗaya. A littafin na uku, Bunayya The Broken Kola, labarin Bunayya ya cigaba, yayin da ta samu  amsoshin tamboyin da suka sarƙafe mata a wannan bincike da take yi. Bunayya ta isa har Sakkwato daga Kano, inda yarda da aminci suka birkice komai. A nan ne komai ya bayyana aka fahimci asalin sirrin da ke ɓoye dangane da wannan ƙwarya da aka yi maganarta a littafin baya. Shi ne kuma zai zama makullin fassarar wannan tsohon rubutun ajami da aka gano. Dukkan amsoshin da aka samo daga wannan binciken da aka yi ya ja ta kusa da mugayen makiyan da suka sha alwashin binne gaskiyar, har ma da ita daga doron kasa bakiɗaya. 

Kashi na huɗu na wannan labari shi ne labari na ƙarshe. An yi wa littafin taken Bunayya, The Lost Soul: The Last Rite. A ciki ne za mu ji yadda Bunayya ta isa Maiduguri domin haɗuwa da ƙalubalen ta na ƙarshe, sakamakon abin daya faru da ita a Zaria zuwa Kano zuwa Sakkwato. Halin da ta shiga ya sa dole sai ta yanke shawarar ta tona gaskiyar abinda ya faru akan abin da ta fi so, ko ta zama ita ce sadaukarwar a cikin yaƙin da aka dade da mantawa. Wannan abu na ƙarshe da za ta yi shi ne zai zama sanadin ta da kuma sanadin tarihin ma bakiɗaya. 

Yaya ki ke fuskantar ƙalubalen kasuwancin littattafanki? Kina mayar da kuɗinki kuwa?

Za mu bayar da wannan amsar a mako na gaba, kafin wasu su biyo baya.

By ukarofi