Rundunar ‘yan sanda ta damƙa wanda ake zargi da safarar hodar iblis ga Birtaniya

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta miƙa wanda ake zargi da hannu a manyan laifuka mai suna Mathew Chukwuemeka Adebiyi ga ƙasar Birtaniya domin ya fuskanci gurfanarwa akan zarge-zargen kisa da safarar miyagun ƙwayoyi.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Anthony Okon Placid ya bayyana haka a wata takarda da ya fitar a ranar Alhamis ta sahihin shafin hukumar na dandalin Facebook.

A cewar sanarwar, an gudanar da haka ne ta Cibiyar ayyukan hukumar ta kula da lamuran ƙasa-da-ƙasa (NCB) a Abuja, bayan buƙatar da hukumomin Ingila suka miƙa a watan Satumbar 2024.

Hukumomin ‘yan sanda sun zargi Adebiyi da hannu a kisan wani Joshua Boadu a ranar 18 ga watan Yunin 2018 a Birtaniya.

Haka kuma ana zargin sa da aikata laifin raba wani nau’in hodar iblis na musamman a tsakanin shekarar 2017 da 2018.

Bayan haka, wanda ake zargin ya tsere zuwa Nijeriya domin guje wa kamu, amma daga bisani a ranar 23 ga watan Junairu, 2025, jami’an INTERPOL na NCB Abuja sun yi ram da shi.

Akan haka ne wata Babbar Kotun Tarayya a Legas ta yanke hukuncin damƙa shi ga hukumomin Birtaniyar domin gudanar da shari’a akansa.

By Babaji