Saraki ya nemi Akpabio ya miƙa wuya ga sahihin bincike kan zargin cin zarafin Natasha

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya yi tsokaci game da batun zargin cin zarafi da Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi akan Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio.

A wata sanarwa da Saraki ya fitar a ranar Asabar, ya koka kan rikicin inda ya ce hakan abu ne da ka iya rage darajar majalisar matuƙar ba a tabbatar da gaskiya da adalci wajen yin hukunci ba a matsayinta na mafi girman reshen gwamnati.

Ya shawarci ɓangarorin biyun da magoya bayansu da su kiyayi ƙalubalen da kalamansu ka iya haifarwa, inda ya yi kira a gare su da su fifita darajar majalisar akan ra’ayoyinsu na kai-da-kai.

Saraki ya kuma yi kira da a tabbatar da bin ƙa’idojin doka da nuna ƙwarewa a yayin warware rikicin, ya na mai kira ga kwamitin kula da sanin makamar aiki da ƙararraki da ya yi adalci a yayin hukunci kan batun.

Haka kuma, Saraki ya yi kira ga Akpabio da Akpoti da su bai wa kwamitin haɗin kai don tabbatar da adalci a yayin hukuncin.

Har’ilayau, Saraki ya yi gargaɗin kada a bar majalisar ta zama fagen da ke sakaci game da batutuwan rashin ladabi da suka ƙunshi cin zarafi da tauye jinsi da cin mutuncin aiki da abubuwa makamantansu.

By Babaji