Shugaba Tinubu ya ɗauko hanyar yalwata ƴan Nijeriya, inji Shettima

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya ce, jagoranci na gari da hangen nesa na Shugaba Bola Tinubu zai taimaka wajen sauya Nijeriya ta fuskar samun ci-gaba a nan gaba.

Ya ce, hakan zai samu ne la’akari da ƙoƙarin da ya ke yi na zuba jari a ƙarƙarshin tsarinsa na sabonta ƙasa a ɓangarorin kiwon lafiya, Ilimi da wasu manyan ababen harkar tattali.

Ya bayyana hakan ne a yayin da ya karɓi baƙoncin tawagar Gidauniyar Big Win Philanthropy kaseta A, ƙarƙashin jagorancin Shugabarta, Jamie Cooper a Fadar Shugaban ƙasa, a Abuja.

Ya kuma marabci buƙatar gidauniyar ta neman yin aiki kafaɗa-da-kafaɗa da gwamnatin Shugaba Tinubu don cimma manufofin Ajendarsa ta Sabonta ƙasa, ya na mai cewa a shirye suke su bada duk haɗin kan da ake buƙata wajen cimma nasara.

Haka kuma, ya bayyana shirin ‘Nutrition 774 Initiative’ a matsayin abinda zai amfani al’umma tun daga mataki na ƙananan hukumomi don yaƙi da rashin samun wadataccen kulawa a ɓangaren lafiya.

A nata jawabin, Shugabar Gidauniyar, Cooper, ta ce sun ziyarci Fadar shugaban ƙasar ne da nufin tattaunawa da mataimakin shugaban ƙasar ganin yadda ya ke taka muhimmiyar rawa a ayyukan inganta ƙasa da al’umma da kuma neman haɗa hannu da gwamnati don cimma kyawawan manufofinta.

By Babaji