Daga GAMBO ISA
Shugaban Ƙaramar Hukumar Fune a jihar Yobe, Hon. Alhaji Baba Goni Mustapha Bade ya rantsar da sabbin zaɓaɓɓun kansiloli 13.
Da yake jawabi a wajen taron da babbar kotun majistare ta gudanar a zauren majalisar da ke Damagum, bisa ga kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya Hon. Baba Goni Mustapha Bade ya miƙa saƙon taya murna ga sabbin zaɓaɓɓun kansilolin, inda ya jaddada muhimmancin ayyukansu, wajen yin aiki tuƙuru da inganta ruhin aiki bisa ƙa’idojin majalisar ƙaramar hukumar da aka kafa.
Wannan taron dai wani gagarumin ci gaba ne a tafiyar ƙaramar hukuma Fune, inda ya yi nuni da irin sadaukarwar da aka yi a lokacin zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar kwanan nan.
Hon. Baba Goni Mustapha Bade ya kuma ce waɗannan naɗe-naɗen sun ba ku wata dama ta ba ku gudummawar wajen tabbatar da gaskiya da sanin ya kamata da kula da dukiyar gwamnati domin ingantacciyar gudanar da ayyukan gwamnatinmu.
Hon Baba Goni Mustapha Bade ya kuma tunatar da sabbin zaɓaɓɓun kansilolin da su yi biyayya ga rantsuwar da suka yi.
Shugaban zartarwar ya kuma jaddada muhimmancin mutunta tsarin jam’iyyar da aka zaɓe su a ƙarƙashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
Hon. Baba Goni Mustapha Bade ya kuma yi wa kansilolin fatan samun nasarar gudanar da aikinsu tare da yi musu addu’ar Allah ya yi musu jagora wajen gudanar da ayyukansu na ci gaban yankin Fune da jihar Yobe.
Hon. Baba Goni Mustapha Bade ya buƙace su da su cigaba da addu’a ga Allah Maɗaukakin Sarki ya dawo mana da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar Yobe da ƙasa baki ɗaya.
A nasa jawabin Hon. Baba Goni Mustapha Bade ya bayyana goyon bayansa ga Gwamna Mai Mala Buni Ciroma Gujba, manufofi, da kira ga al’umma da su hada kai da manufofin gwamna da manufofinsa.”
An rufe bikin tare da Hon. Baba Goni Mustapha Bade yana yi wa kowa fatan alkhairi da fatan Allah ya dawo mana da shi gida lafiya, yana mai roƙon Allah ya saka masa da mafificin alkhairi.
