Daga UMAR M. GOMBE
Sojojin Nijeriya tare da haɗin gwiwar takwarorinsu sun soma gudanar da bincike domin gano ‘yan bindigar da suka kashe Manjo Janar Hassan Ahmed kwannan nan a Abuja.
Jami’an sun soma binciken ne a yankin Koton Ƙarfe a jihar Kogi.
An yi zargin wasu ‘yan bindiga ne daga Koton Karfe suka harbe marigayin a kan hanyarsa ta komawa Abuja daga jihar Kogi.
Yayin harin ‘yan bindigar sun tafi da wata ‘yar’uwar marigayin wadda suke tare da ita a cikin motarsa, yayin da direbansa kuwa ya tsallake rijiya da baya.
A juma’ar da ta gabata aka yi jana’izar Manjo Hassan a maƙabatar sosoji da ke Barikin Lungi a Abuja.
Bayanai sun nuna Koton Ƙarfe na daga cikin yankunan da suka yi ƙaurin suna wajen harkokin ‘yan bindiga da garkuwa da mutane da sauran muggan laifuka.