Tinubu ya jinjina wa Hadiza Bala Usman a zagayowar ranar haihuwarta

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Mai Girma Shugaba Bola Tinubu ya yaba wa Hadiza Bala Usman, wato mai ba sa shawara na musamman akan tsare-tsaren harkokin gwamnati kuma Shugabar Cibiyar Isar da Sakamakon Tsare-tsare (CRDCU) bisa gagarumar gudumawarta ga hidimar ƙasa yayin da take cika shekaru 50 a duniya.

A wata sanarwa da Kakakin Shugaban Ƙasa Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana Hadiza a matsayin “jajirtacciyar mai kishin ƙasa” wadda aikinta na kusan shekaru 30 a gwamnati ya zama abin misali ga al’umma sakamakon sadaukarwa da himmarta ga ci-gaban ƙasa.

Shugaban ƙasar ya kuma yaba wa ƙoƙarinta na aiki a Hukumar kula da kadarorin gwamnati inda ta nuna hangen nesa da fahimta na daidai ga muhimman gyare-gyaren tsarin ci-gaban harkar tattali.

Haka kuma ya yaba wa gudumawarta na Hukumar Kula da kadarorin birnin tarayya, yana mai bayyana hakan a matsayin babban mataki ga zangon aikinta inda ta nuna ƙwarewa wajen kiyaye gaskiya da adalci ga harkokin al’umma.

Kazalika, Tinubu ya yabi hidimarta a harkar siyasa musamman cikin jam’iyyar APC wajen shirye-shirye da harkokin ci-gaba, lamarin da ya taimaka wajen inganta lamuranta na cikin gida da ƙarfafa darajojin dimukraɗiyya.

A ƙarshe, ya kammala da yi mata fatan cigaba da samu ƙwarin gwiwa, hikima, lafiya da ikon tafiyar da al’amuran ayyukanta, waɗanda abin kwaikwayo ne ga mata, matasa da kuma jagororin ƙasa.

By ukarofi