Trump ya bayyana yiwuwar ya tsaya wa takara a karo na uku

Spread the love

Shugaban Amurka Donald Trump ya ƙi yin watsi da yiwuwar neman wa’adi na uku akan karagar mulki, duk kuwa da dokar da kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada.

A wata hira ta musamman da NBC News, Trump ya bayar da shawarar cewa akwai hanyoyin da za a cimma hakan, yana mai jaddada cewa “ba wasa ba ne.”

Kalaman nasa sun yi nuni da tsarin siyasa a wasu ƙasashe masu tasowa da ke da irin wannan tsarin- tsarin da Amurka ta sha suka a baya.

“Mutane da yawa suna son in yi hakan,” inji Trump yayin wata tattaunawa ta wayar tarho, yayin da yake magana kan magoya bayansa. “Amma Ina gaya musu mun yi saurin ɗauko wannan zamce a gwamnatina.”

Da aka matsa masa kan ko da gaske ne ya nemi wani wa’adi, Trump ya amsa da cewa, “Ina son yin aiki, ba wasa nake ba,” amma ya ƙara da cewa “ba lokacin da ya kamata ya fara wannan tunanin ba ne.”

Dangane da ko an gabatar masa da dabarun da za a iya wa’adi na uku, Trump ya ce, “Akwai hanyoyin da za a iya yi.” Sai dai ya ƙi yin ƙarin bayani lokacin da aka tambaye shi cikakken bayani.

Wata shawara da aka gabatar yayin hirar ita ce, ta Mataimakin Shugaban ƙasa JD ɓance zai iya tsaya wa takarar shugabancin ƙasar sannan daga baya ya miƙa mulki ga Trump. Da yake mayar da martani, Trump ya ce, “Wannan ɗaya ce daga hanyoyin da za a iya bi,” amma ya yi ishara da wasu hanyoyin da za a iya bi ba tare da bayyana su ba.

A ƙarƙashin Kundin Tsarin Mulki na Amurka na 22, shugaban ƙasa yana iyakance ga wa’adi biyu. Juyar da wannan doka zai buƙaci ko dai kashi biyu bisa uku na ƙuri’a a majalisa ko kuma goyon bayan kashi biyu bisa uku na jihohin Amurka don gudanar da babban taron tsarin mulki, sannan a amince da kashi uku bisa huɗu na jihohin.

Duk da cikas da kundin tsarin mulkin ƙasar ke da shi, Trump ya yi nuni da yawan ƙuri’unsa masu ƙarfi, yana mai jaddada cewa Amurkawa da dama za su mara masa baya ya sake yin wani wa’adi.

Wannan dai ba shi ne karon farko da Trump ya yi tsokaci game da wa’adi na uku ba. Yayin da wasu ‘yan jam’iyyar Republican suka yi watsi da irin waɗannan kalamai inda suka ba su muhalli a matsayin barkwanci, wasu kuma da alama suna ɗaukar su da muhimmanci.

A wani labarin kuma, ɗan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican Andy Ogles a baya-bayan nan ya gabatar da wani ƙuduri na neman tsawaita wa’adin mulkin shugaban ƙasa, wanda ka iya ba wa Trump damar ya sake tsayawa takara.

A halin da ake ciki kuma, na kusa da Trump, Steɓe Bannon, ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa Trump zai sake tsayawa takara kuma ya sake lashe zaɓen shugaban ƙasa a shekara ta 2028. Da yake magana a wata hira da News Nation, Bannon ya yi iƙirarin cewa akwai “hanyoyi daban-daban” da za su ba wa Trump damar ya yi fiye da wa’adi biyu.

Wani mataki da ya ƙara rura wutar hasashe, kwanan nan fadar White House ta yaɗa wani hoto a shafukan sada zumunta da ke nuna Trump da kambi, biyo bayan ƙin amincewa da farashin cunkoson da gwamnatinsa ta yi a birnin New York. Rubutun a kan ɗ ya nakalto bayanin da Trump ya yi a shafinsa na The Truth, wato “Allah Ya ja zamanin Sarki!”

Kalaman na Trump da martanin da suka haifar na ci gaba da haifar da mahawara, inda masu sharhi kan al’amuran siyasa suka sanya ido sosai kan lamarin.

By ukarofi