Tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Ibrahim Mantu ya kwanta dama

Spread the love

Allah Ya yi wa tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Ibrahim Nasiru Mantu.

Bayanai sun nuna marigayin ya rasu ne a cikin daren Litinin a wata asibitin Abuja bayan fama da rashin lafiya.

A halin rayuwarsa, marigayin cikakken ɗan siyasa ne, kuma tsohon sanata da ya wakilci Filato ta Tsakiya a Majalisar Dattawa. An zaɓe shi a matsayin sanata ne 1999 inda ya zama mataimakin shugaban Majalisar a shekarar 2000.

Baya ga haka, Mantu ya yi aiki a wurare da dama tare da riƙe muƙamai daban-daban inda ya ba da tasa gudunmawa ga cigaban ƙasa.

An haifi Mantu ne a ranar 16 ga Fabrairun 1947 a jihar Filato inda ya bar duniya yana da shekara 74.

By Editor