Tare da ABDULHAMID Na MATAZU
- Da Sunan Allah na Mai Girma,
Baitochi ne Zan Tsara ma. - Mabuwayi Kuma Gagara Gasa,
WANZAJJE tun Kan Kowa Ma. - Bai Haifa Ba Ba a Haifai Ba,
bai da KINI Allah mai ‘AMA. - Shi ne yake Da Mulkin Sammai,
har ƙassai Shi sarkin Girma. - Shi ne Muke Nufa Da Buƙata,
duk kuma Shi ne zai yaye ma. - Allah Shi ke Ba mu ISASSA,
Shi ke Kawo Har MARDHUN ma. - Sai dai duk CUTAR da Dawa’i,
in Yaga Dama Yayyaye ma. - Jallah Ya Ba mu Abincin cin mu,
dats tsuntsaye Dabbobi ma. - Shi yai ZAKI shi yai KURA,
CINNAKA sauro Da Kunama. - Mai ƊACI bauri Daz ZAQI,
Har Hamami Tuni na Sallamma. - Shi ya Kamata Ayi wa BAUTA,
Shi Daya RAK sam Ba a Haɗi ma. - Yi Mai Tarayya ce SHIRKA,
Bai Karɓa Ranar Ƙiyyama. - In Ka Bi shi Anan Kai Sa’a,
lahirra can Ba bu Nadama. - Baka Shiga Wuttar Hawiyya,
a Lahirar Balle su Huɗama. - Abdulhammid Ni NaMATAZU,
Nayyo Kan Allah Mai Rahma.