
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Babban Kamfanin Raba Wutar Lantarki na Ƙasa TCN, ya sanar da cewa za a samu tsaiko yayin raba wuta a wasu yankunan birnin tarayya Abuja har na tsawon makonni biyu.
Kakakin kamfanin, Ndidi Mbah ya sanar da haka a wata takarda ranar Litinin.
A cewar TCN, tsaikon zai samu ne sakamakon aikin gina titina da ake yi, wanda zai faru tun daga yau Talata, 28 ga watan Oktoba zuwa Nuwamba 16.
Ya ce, a yayin haka za a rasa wuta a layin Gwagwalada-Kukwaba-Apo mai nauyin kilovolt 132, wato ninki biyu na layin lantarki.
Don haka za a samu ɗaukewar wuta a yankunan Apo, Lokogoma, Guzape, Asokoro, Wuye, Utako, Jabi da Idu Industrial Layout.
Sanarwar ta ƙara da cewa, za a riƙa samar da wuta a yankunan ne a yayin da aka gama aikin kowace rana domin rage musu matsin da hakan ka iya haifar musu.
