Musulmi a Nijeriya da sauran sassan duniya sun fara azumin watan Ramadana na shekarar 1447AH/2026 bayan sanarwar da Shugaban Majalisar ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Nijeriya (NSCIA) kuma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya fitar bayan tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan.
Sanarwar ta biyo bayan rahotannin kwamitocin ganin wata na jihohi daban-daban da kuma tantancewar kwamitin ganin wata na ƙasa. Kamar yadda shari’ar Musulunci ta tanada, ganin jinjirin watan Ramadan ke nuna ƙarshen watan Sha’aban da kuma fara azumi.
A saƙonsa, Sarkin Musulmi ya jaddada muhimmancin amfani da wannan wata wajen ƙarfafa zaman lafiya, hadin kai da addu’o’i ga ƙasa. Ya buƙaci gwamnati ta ƙara himma wajen magance matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke addabar al’umma, tare da kira ga Musulmi su mayar da hankali ga ibada, sadaka da kyautatawa juna.
Yin azumin watan Ramadan a wata na tara na kalandar Musulunci na ɗaya daga cikin ƙa’idoji biyar na Musulunci waɗanda idan ba yi su ba imanin mutum ga addinin Musulunci zai kasance bai cika ba.
A Musulunci, azumin Ramadan ya ƙunshi kamewa daga ci, sha, shan taba, tsakanin alfijir da faɗuwar rana na tsawon watan Ramadan. Umurnin wannan farilla na addini yana cikin Alkur’ani sura 2:183 inda Allah Maɗaukakin Sarki ya ke cewa, “Ya ku waɗanda suka yi imani! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke a gabaninku, tsammaninku. Ana azumin watan Ramadan na kwanaki 29 ko 30, gwargwadon lokacin da aka ga jinjirin watan Shawwal, wata na goma a kalandar Musulunci.
Baya ga nisantar abinci a jiki baya ga wasu hane-hane da aka yi wa muminai a lokacin azumin watan Ramadan, an kuma umurci musulmi da su yi amfani da wannan lokaci mai alfarma wajen nuna kyawawan halaye na haƙuri da karimci da sadaka da kyautatawa musamman ga marasa galihu a cikin al’umma.
Don haka ake kwaɗaitar da su da yin sadaka, ciyar da miskinai da kuma kiran sauran waɗanda ba musulmi ba domin buɗa baki da su. Aikin alherin da ake yi a watan Ramadan yana samar da ingantacciyar fahimta ta addini, daidaito da kuma haɗin kan al’umma, waɗanda dukkansu sun fi so ga al’umma masu yawan imani da mabanbantan ra’ayi irin Nijeriya.
Azumin Ramadan yana bai wa mumini na kwarai haƙuri da juriya. Idan musulmi ya yi azumi, yana iya jin raɗaɗin yunwa ko ƙishin ruwa amma a haƙura. Wannan raɗaɗi da juriya, ko da ya ke na ɗan lokaci ne, suna sa mutum ya san irin halin da wasu da yawa ke fama da su, waɗanda wataƙila suna rayuwa a cikin ƙunci tare da ƙarancin samun abubuwan buƙatun rayuwa.
Jigon wannan wata yana buƙatar Musulmi da su yi tawali’u a cikin duk abin da suka shagaltu da su. An ƙarfafa su da kada su ci abinci kuma su kiyaye faɗi kuma su kwana cikin ibada. Ya kamata al’ummar Musulmi a Nijeriya a matsayinsu na shugabanni, su yi amfani da damar da watan Ramadan ke da shi wajen nisantar duk wata munanan ɗabi’u da ta addabi ƙasar nan da kawo cikas ga burinta na zama mai ɗogaro da kai da cigaban gaske.
Muna kira ga malamai da masu wa’azi da su kasance masu gaskiya ga kiran da suke yi a matsayinsu na shugabanni a cikin al’umma, da sauran masu kula da yanayi na musamman a ƙasar. A nisanci kalamai ko maganganu masu zafi da tunzura a cikin tafsirinsu na Alkur’ani da sauran littattafan addini. Kyakyawar wa’azi a Musulunci yana buƙatar a yi amfani da hikima da kalmomi masu kyau. An shawarci masu wa’azi da su ilimantar da masu sauraronsu a kan kyawawan halaye na amfani da hanyoyin da ba na tashin hankali ba don samar da zaman lafiya mai ɗorawa a ƙasar.
Ramadan yana kira ga barin kwaɗayi. Muna kira ga dillalan kayan masarufi da kada su yi amfani da lokacin Ramadana da bai kamata ba wajen cin riba ta hanyar ƙara farashin kayan abinci wanda tuni ya kankama.
Blueprint Manhaja na yi wa ɗaukacin al’ummar Musulmi barka da azumin watan Ramadana
