
Gwamnatin Tarayya ta ce kaso na farko na ’yan Nijeriya da aka kwaso daga Afirka ta Kudu sakamakon hare-haren ɓangaranci da ƙyamar baƙi ya isa Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas da safiyar yau Alhamis.
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, inda ya ce ana sa ran jirgin zai sauka da misalin ƙarfe 5:00 na safe.
Sanarwar ta ce jirgin kamfanin sufurin jiragen sama na Air Peace zai tashi daga Filin Jirgin Sama na Oliver Tambo da ke Johannesburg a daren ranar Laraba.
Ebienfa ya ce Gwamnatin Tarayya ce ta ɗauki nauyin gudanar da aikin kwaso mutanen gaba ɗaya, tare da shirya duk wasu matakan tarba da tallafin da za a bai wa waɗanda za su dawo gida.
Ya ƙara da cewa da zarar sun isa Nijeriya, za a yi musu rajista da tantancewa kafin a ba su tallafin da ya dace sannan a haɗa su da iyalansu.
Tun da farko an shirya fara jigilar mutanen ne a ranar Litinin, amma daga baya aka ɗaga zuwa Laraba saboda wasu matsalolin shirye-shirye da suka taso.
