Ziyarar Katsina: Tinubu ya ci alwashin kammala titin jirgin ƙasa na Kano zuwa Maraɗi

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Shugaba Bola Tinubu ya ce, Gwamnatin Tarayya ta shirya kammala aikin titin jirgin ƙasa mai tsawon kilomita 284, wanda ake ginawa a Kano – Jigawa – Katsina – Maraɗi, zuwa nan da shekarar 2026.

Ya bayyana hakan ne a Jihar Katsina, a lokacin da ya ke ƙaddamar da Cibiyar Harkokin Noma ta Katsina da kuma titin yanke mai tsawon kilomita 24 dake yankin Tashar Bala a jihar.

Shugaba Tinubu ya ce, titin jirgin, wanda ya kama daga Kano zuwa Maraɗi a ƙasar Nijar, zai taimaka wajen sauƙaƙe harkokin sufuri ga mutane da kayayyakin kasuwanci a shiyyar Arewa maso Gabashin Nijeriya.

Ya kuma ce, sun bada kwangilolin gyaran titunan Mararraban Ƙanƙara – Dutsinma – Katsina da na Zariya zuwa Hunƙuyi zuwa Dabai da kuma na Ƙafur zuwa Malumfashi zuwa Dayi da gidan Mutum Ɗaya.

Ya ƙara da cewa, a yanzu ana cigaba da zango na biyu na aikin titin Katsina biyo bayan da Gwamnatin Tarayya ta warware matsalolin da suka haifar da cikas a baya.

By Babaji