
Daga BELLO A. BABAJI
Ɗaya daga cikin manyan ƙasa kuma shahararren ɗan kasuwa, Alhaji Alhasan Aminu Ɗantata ya bada tallafin Naira biliyan 1.5 ga waɗanda ambaliyar Maiduguri, babban birnin jihar Borno ta rutsa da su.
Ɗantata wanda ya jagoranci tawaga daga Jihar Kano, ya bada tallafin ne a lokacin da ya kai ziyara Fadar gwamnatin Borno inda ya jajenta wa gwamna Babagana Zulum da mutanen musamman waɗanda suka rasa makusantansu.
Attajirin ɗan kasuwar mai shekaru 96, ya bayyana yadda tattalin arziƙin ƙasa ya shiga wani hali, ya na mai kira ga masana da ƴan siyasa su tuba kuma su ji tsoron Allah a yayin jagorantar al’umma.
Ya kuma yi addu’ar samun zaman lafiya mai ɗorewa ga jihar da ma ƙasa baki ɗaya.
A lokacin da ya ke magana, Gwamna Babagana, ya yi farin ciki da zuwan attajirin tare da yi masa godiya bisa ga kyautatawarsa a gare su, ya na mai masa fatan samun kyakkyawar ƙarshe.
Hakan na zuwa ne bayan da ɗa a gare shi kuma sannen Attajiri, Alhaji Aliko Ɗangote ya bada tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda ambaliyar ta shafa.
