
Daga BELLO A. BABAJI
Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Muhammad Matawalle MON ya sanar da samar da Cibiyar Na’urorin Bin diddigi ta ƙasa-da-ƙasa reshen Yammacin Afirka wanda Hukumar Yankunan Ruwa ta Ƙasa za ta jaogranta.
Matawalle ya faɗi haka ne a taron Ranar Yankunan Ruwa ta Duniya ta 2025 da aka yi a Abuja.
Ya ce, za a yi hakan ne da nufin inganta ayyuka ya yankunan da ƙarfafa alaƙa a tsakanin ƙasashen da ke shiyyar domin ciyar da ɓangaren gaba.
Ya kuma ce, Gwamnatin Tarayya tana aiki tuƙuru wajen ganin ta inganta tsaro a tashoshin ruwan Nijeriya da kulawa da albarkatunta.
Haka kuma, sabuwar cibiyar za ta sanya Nijeriya ta zama kan gaba wajen amfani da ababen ci-gaba na zamani da jagorancin harkar gaɓar ruwa a yammacin Afirka da ma sama da haka.
Ministan ya bayyana cewa, cibiyar za ta taimaka wajen bunƙasa harkokin tattalin arziƙi ta hanyar faɗaɗa ayyukan tashoshin jiragen ruwa da makamantansu.
