Bayanan da suka cim mana na nuni da cewa, tsohon Shugaban Hukunar EFCC, Ibrahim Lamorde, ya kwanta dama.
Majiyarmu ta ce marigayin ya rasu ne a ƙasar Masar inda ya tafi jinya, kuma ya bar duniya yana da shekara 61.
An haifi marigayin ne a ranar 20 ga Disamban 1962, sannan ya shiga aikin ɗan sanda a 1986 inda ya yi ritaya a matsayin Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda 2021.
A halin rayuwarsa, ya riƙe muƙamin Shugaban EFCC daga 2011 zuwa 2015 bayan da Shugaba Goodluck Jonathan ya tsige Farida Waziri a muƙamin shugabancin hukumar.
