Shugaba Tinubu zai yi ma yan Najeriya Jawabi ranar dimukraɗiya da misalin 7am ranar Laraba.
Mai baiwa Shugaban ƙasar shawara Ajuri Ngelale ne ya sanar da hakan a wani bayani da ya fitar ranar Talata a Abuja.
Wani sashen bayanin yana cewa ” Gidajen talabijin da rediyo da duk wasu kafofin yaɗa labarai su nemi jawabin ta hanyar gidan talabijin na ƙasa wato NTA da kuma FRCN”
