
Daga BELLO A. BABAJI
Gwamnatin Tarayya ta aika da saƙon gargaɗi ga al’umma kan mamakon ruwan sama da za a fuskanta na tsawon kwanaki biyar masu zuwa waɗanda hakan ka iya haifar da ambaliya a jihohi guda 21.
Cibiyar aika Gargaɗin Ambaliya ta Ƙasa ƙarƙashin Ma’aikatar Kula da Muhalli ta bayyana haka a ranar Alhamis inda ta ce ana tsammanin hakan ya kasance daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Satumba.
Ta yi hasashen ruwan saman zai iya sa a samu ambaliya a wurare 123 cikin jihohin da aka lissafa.
Ta kuma bada shawara ga al’umma da ke garuruwan kusa da ruwan ‘River Benue’ su gaggauta barin yankunan saboda akwai yiwuwar a samu ambaliya.
Jihohin da ake tsammanin samun ambaliya sune; Adamawa, Benue, Bauchi, Kogi, Borno, Nasarawa, Gombe, Kwara, Jigawa, Oyo, Kaduna, Edo, Kano, Katsina, Kebb, Plateau, Neja, Sakkwato, Taraba, Yobe da kuma Zamfara.
Hukumomi sun yi kira ga al’umma su kasance masu lura da kuma ɗaukar matakan kariya ga rayuka da dukiyoyinsu.
