
Daga BELLO A. BABAJI
Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta sanar da cewa ɓarayi a intanet sun datse adireshinta na yanar gizo.
A ranar Laraba ne hukumar ta wallafa hakan a shafinta na X.
Ta yi kira ga al’umma da ƙaurace wa duk wani bayani da za a yaɗa a ƙafar daga yanzu har zuwa lokacin da za a kammala aikin gyaran adireshin.
A halin yanzu jami’an gudanarwa suna ƙoƙari wajen ganin shafin ya koma aiki yadda aka saba kamar yadda suka tabbatar a sanarwar.
