Sirrin da ya sa Gwamna Bala sukar ƙudirin harajin Tinubu – Minista

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya yi ikirarin cewa Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi yana amfani da sukar Shugaba Bola Tinubu kan dokar sabuwar haraji da sauran manufofinsa wajen ƙaddamar da ƙudirinsa na tsayawa takarar shugabancin ƙasa a 2027.

Ministan ya yi wannan zargin ne a lokacin da ya bayyana a shirin Siyasa na Lahadi na gidan Talabijin na Channels a ranar Lahadi.

A cewarsa, gwamnan jihar Bauchi ya nuna cewa ba shi da gaskiya a batun sukar da yake yi wa shugaba Tinubu.

“Gwamna Bala Mohammed ya nuna a fili cewa ba shi da wata manufa ta gaskiya,” inji Tugar a cikin shirin.

“Ba wai wasu gwamnoni ba ne suka yi ƙoƙarin yi wa dokar haraji tambayoyi a lokacin da aka gabatar da shi wanda abu ne mai kyau a ka’ida ta yadda ‘yan Nijeriya za su samu nasara a cikin ƙudirin, amma abin da Bala Mohammed ya ci gaba da yi shi ne yin amfani da shi a matsayin wani dandali na ƙaddamar da yaƙin neman zabensa na shugaban kasa da sassafe.

“Ya kasance mafi tsanani a cikin maganganunsa ga shugaban kasa, game da gwamnati tare da goyon bayansa ga shugaban ƙasa da gwamnati.”

Ministan ya ce Gwamna Mohammed ya yi ta ƙoƙarin ganin ya samu jama’a tare da Tinubu biyo bayan sukar da ya yi wa shugaban ƙasa kan audirin gyara haraji.

Gwamnan jihar Bauchi ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga mabiya addinin Kirista a ranar ‘Boɗing Day’ a Bauchi, ya buƙaci shugaba Tinubu da ya ja da baya kan yadda ake sauye-sauyen tsarin haraji domin hakan na iya haifar da rikici.

A cewarsa, ko ta yaya manufar ba ta son Arewa, yana mai cewa gwamnonin ba za su iya biyan albashi ba.

Ya yi gargaɗin cewa idan aka ci gaba da wadannan tsare-tsare, yankin arewa zai “nuna ainihin launukansa” don mayar da martani.

Sai dai fadar shugaban ƙasar ta mayar da martani ga gwamnan tare da yin Allah wadai da abin da ta bayyana a matsayin barazana ga shugaban. Ta ce ra’ayin Mohammed bai yi daidai da ra’ayin Arewa baki ɗaya ba.

By ukarofi