A kafafen sada zumunta muka ga majalisa ta buƙaci mu gabatar da kasafin kuɗi cikin sa’o’i 48 – Gwamnatin Ribas

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Gwamnatin Jihar Ribas ta ce har yanzu ba ta samu ƙudurorin Majalisar Dokokin jihar ba game da hukuncin da Kotun ƙoli ta yanke ranar 28 ga Fabrairu, 2025.

A ranar Litinin, Rt. Hon. Majalisar da Martins Amaewhule ke jagoranta a zamanta ta baiwa Gwamna Siminalayi Fubara wa’adin sa’o’i 48 ya gabatar da kasafin kuɗin jihar na 2025 a gabanta.

A cikin wata wasiƙa da ta aike wa shugaban majalisar mai ɗauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Dr Tammy Danagogo, gwamnatin ta bayyana cewa har zuwa ƙarshen lokacin aiki a ranar 4 ga watan Maris, ofishin gwamna, mataimakin gwamna, ko ofishin Babban Akanta Janar ba su karɓi takardar ba.

Sai dai wasiƙar ba ta bayyana wani mutum da sunan sa a matsayin shugaban majalisar dokokin jihar Ribas ba.

Danagogo ya yi tsokaci kan shirin da Gwamna Siminalayi Fubara ya watsa a jihar kwanan nan a ranar 2 ga Maris, inda ya jaddada ƙudirinsa na mutunta doka.

Ya ce duk da wani ra’ayi na kansa kan hukuncin Kotun Koli, Gwamnan ya tabbatar wa al’ummar Jihar Ribas cewa gwamnatinsa za ta bi tare da aiwatar da hukuncin da kotun ta yanke domin amfanin jihar.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa har yanzu tawagar lauyoyin ta na dakon kwafin gaskiya na hukuncin, kuma ta tabbatar wa da jama’a cewa da zarar sun samu, gwamnan zai yi hakan ba tare da ɓata lokaci ba.

By ukarofi