
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Jagorancin Ƙungiyar Ƙasashe masu Tattalin Arziƙi ta Yammacin Afirka (ECOWAS) gq Nijeriyar ka iya zuwa ƙarshe a yayin da Shugaba Bola Tinubu zai kammala wa’adinsa na biyu a ƴan kwanakin nan.
Za a gudanar da taron ne a ɗakin taro na Banquet Hall dake Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja.
A ranar 9 ga watan Yulin 2023 ne a Guinea Bissau aka zaɓi Tinubu matsayin shugaban ECOWAS, wanda kuma aka sake zaɓar sa a ranar 7 ga watan Yuli, 2024.
Ministan Harkokin Waje, Amb Yusuf Tuggar ya bayyana hakan a taron Majalisar Ministocin ECOWAS karo na 94, ranar Juma’a.
Ya ce, akwai yiwuwar taron ya zama na ƙarshe a gare shi a matsayinsa na jagora, don ya mika godiyarsa ga mambobinta.
Ya kuma yaba wa takwarorinsa bisa gudumawarsu da haɗin kai da suka bayar wajen ciyar da ƙungiyar gaba.
