
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Tsohon Ministan Noma da Raya Karkara, Cif Audu Ogbeh ya rasu bayan shafe shekaru 78 a duniya.
Marigayin ya rasu ne a yau Asabar 9 ga watan Agusta, 2025.
A wata sanarwa daga makusantansa, za a sanar da lokacin gudanar da jana’izarsa.
Sun bayyana godiyarsu ga abokai, abokan aiki da masu fatan alheri a yayin jimamin rashin.
Ogbeh shi ne shugaban jam’iyyar PDP daga shekarar 2001 zuwa 2005, sannan minista ne a zamanin mulkin marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.
Haka kuma shi ne ministan sadarwa a zamanin mulkin marigayi tsohon shugaban ƙasa Shehu Shagari daga 1982 zuwa 1983.
Bugu da ƙari, ya taɓa riƙe muƙamin mataimakin kakakin majalisar dokoki ta Benuwai a ƙarshen shekarun 70s.
