Daga ABUBAKAR LABARAN a Kafanchan
Shugaban ƙaraman Hukumar Jema’a dake jihar Kaduna Honarabul Peter Tanko Dogara ya jaddada ƙudirinsa na aiwatar ta ayyukan gina al’umma waɗanda suka fi buƙata.
Tanko ya yi wannan albishir ne lokacin da ya jagoranci wani taron gangami na mahawara da al’umman ƙaraman hukumar a Kafanchan.
Lokacin da yake bada muhimmanci akan gina karkara, wadda ya ce ita ce abin da gwamnatinsa tafi bada himma akai, shugaban ƙaramar hukuman ya ƙara da cewa, ba zai taɓa ƙasa a gwiwa ba, na tabbatar da ya aiwatar da ayyukan walwala da jin daɗin rayuwa a ko’ina cikin al’umman ƙaramar hukumar Jama’a.
Ya ci gaba da cewa, zai tabbatar ya ba muryar al’umma fifiko domin su faɗi buƙatun su saboda ya yi aiki dai dai da ƙudurorin mai girma Gwamnan jihar Kaduna Sanata Uba Sani.
Tanko ya yi bayani akan ayyukan ci gaba da ya kawo wa ƙaramar Hukumar Jama’a a watanni tara da ya kai a mulki domin kafa matashiyan kawo ci gaba.
Ya yi bayani akan ayyukan gina al’umma da ya aiwatar waɗanda suka haɗa da, kawo wutar lantarki a garuruwan Unguwan Jibrin, Golkofa da Gada biyu.
Ya ƙara da cewa, sauran ayyukan sun haɗa da kwaskwariman Makarantun Firamare na Unguwan Mission, Unguwan Madaki, Unguwan Lamba, Ngaskiya da Zankan sa’annan da kuma kwaskwariman Sakatariyan ƙaramar hukuma da kuma wasu ayyuka.
Shugaban ƙaramar hukuman ya ce “Mun samar wa mabuƙata 30 aiki da kuma makarantu a Jami’ar aikin gona ta Mubi.”
Ya ƙara da cewa, “mun ba kusa da matasa dubu ɗaya jari, bayan sun kammalla horon koyon sana’o’i daga gidauniyar Jennifer Etuh tare da wasu gidauniyoyi.”
Shugaban ya gode wa dukkan al’umman ƙaramar hukumar Jama’a saboda haƙuri da addu’o’insu da kuma goyon bayan da suke ba shi da majalisansa, wanda ya ce shine yake ba shi ƙwarin gwiwan aikata abinda ke kawo ci gaban ƙaramar hukumar.
A jawabinsa a farkon taron, shugaban sashen kasafin kuɗi na ƙaramar hukumar, John Samson ya bayyana dalilin shirya taron domin a samar wa al’umman ƙaramar hukumar dama, su gabatar da ayyukan da suke buƙatan ƙaramar hukumar ta aiwatar musu a kasafin kuɗi na shekara mai zuwa.
Samson ya yi la’akari da cewa buƙatu da gudunmawar al’umman zai taimaka wa ƙaramar hukumar cimma burinta na aiwatar da ayyukan kasafin kuɗin baɗi cikin nasara.
Taron wanda ta haɗa da sarakuna, shuwagabannin addinai, ƙungiyar mata da ƙungiyoyin mata, ya baiwa masu fada aji daman su fadi ra’a’yoyin su dangane da abubuwan ci gaba da suke buƙata a garuruwansu a cikin kasafin kuɗin shekara mai zuwa.
