Gwamnan Katsina ya sanya dokar ta-ɓaci kan ƙauraye a Katsina

Spread the love

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya sanya hannu kan dokar ta-ɓaci kan ‘yan ƙauraye da yan bangar siyasa a cikin garin Katsina.

Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa kafa wannan doka ya biyo bayan ƙaruwar faɗace faɗacen ƙauraye da yawaitar bangar siyasa a faɗin jihar musamman cikin garin Katsina.

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan ya kuma bayar da umarnin a riƙa hukunta duk wanda aka kama da aikata irin wannan laifi nan take.

Matakin na zuwa ne a wani yunƙuri na gwamnatin jihar na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a cikin birnin Katsina.

By ukarofi