Daga IBRAHIM HAMISU a Kano
Babbar kotun ƙolin Najeriya ta saka ranar 19 ga watan Aprilun 2027 domin ci gaba da shari’ar masarautar Kano.
Kotun ta sanya ranar ne domin saurare tare da karɓar martanin waɗanda aka yi ƙara a shari’ar wadda Alhaji Aminu Babba Ɗan Agundi ya shigar gabanta.
Kazalika, mai ƙarar yana ƙalubalantar hana shi damar da doka ta ba shi a matsayinsa na babban ɗan majalisar sarki wanda majalisar dokokin Kano ta yi ta hanyar sauya dokar masarautu.
Wannan shari’ar dai ta nuna cewa sai bayan shekara guda za’a cigaba da shari’ar.
