Daga IBRAHIM HAMISU a Kano
Jirgin farko na alhazan jihar Kano ya tashi zuwa Saudi Arabia domin gudanar da ibadar hajjin bana.
Rukunin farko na alhazan 558 ya tashi ne a jirgin Max Air daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano zuwa birnin Madinah da misalin ƙarfe 12:48 na dare a yau Asabar, 16/05/2026.
Rahotanni sun nuna cewa alhazan sun isa Filin jirgin Madina da misalin ƙarfe 7:35 na safe.
A cikin maniyata 558 da suka tashi 333 maza ne sai mata 225.
Kazalika, alhazan da suka tafi sun fito ne daga ƙananan hukumomi Dala, Gwale Ungoggo da kuma Fagge.
