Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a katsina
Gwamnatin Jihar Katsina ta ayyana ranar Talata, 16 ga Yuni, 2026 a matsayin ranar hutu domin bikin fara shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1448AH (1 ga Muharram).
Kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na jihar, Dakta Bala Salisu Zango, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Litinin.
Gwamnan ya buƙaci al’ummar jihar su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’o’i da tunani domin samun zaman lafiya, ci gaba da wadata ga Jihar Katsina da Nijeriya baki ɗaya.
