‘Yan Nijeriya na cikin ƙunci – Rufai ya mayar wa Onanuga martani

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja 

Fitaccen mai gabatar da shirye-shirye na gidan talabijin na Arise TV, Rufai Oseni, ya soki Mai Bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, bisa kalamansa da ke nuna cewa rahotannin da ke bayyana tsananin yunwa da wahalar rayuwa a Nijeriya sun wuce gona da iri.

Da yake magana a shirin The Morning Show na Arise Television a ranar Laraba, Rufai ya ƙalubalanci Onanuga da ya fito fili ya rantse cewa yawan ’yan Nijeriya da ke neman taimakon kuɗi daga gare shi bai ƙaru ba tun bayan hawan gwamnatin Tinubu a watan Mayun 2023.

Rufai ya bayyana cewa kalaman Onanuga sun nuna kamar bai fahimci irin matsin tattalin arzikin da talakawan Nijeriya ke ciki ba.

“Bayo Onanuga ya rantse da Alƙur’ani ko Littafi Mai Tsarki cewa yawan mutanen da ke roƙon sa a ba su Naira 2,000 domin biyan buƙatu na gaggawa bai ƙaru ba tun bayan zuwan gwamnatin Tinubu,” inji Rufai.

Ya ce ƙaruwa da ake samu wajen neman taimakon kuɗi domin biyan buƙatun yau da kullum wata alama ce ta irin ƙalubalen tattalin arzikin da iyalai da dama ke fuskanta a faɗin ƙasar nan.

Kalaman Rufai sun zo ne bayan wata hira da Onanuga ya yi a baya, inda ya bayyana cewa bai yarda da ikirarin da wasu ke yi na cewa yunwa da wahalar rayuwa sun yi muni a Nijeriya kamar yadda ake yaɗawa ba.

A cewar Onanuga, gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da shirye-shirye da dama domin rage raɗaɗin matsin tattalin arziki da inganta rayuwar al’umma. Ya ambaci manyan ayyukan more rayuwa, shirin bayar da lamunin karatu ga ɗalibai da kuma rancen kuɗi ga ma’aikata a matsayin wasu daga cikin matakan da gwamnati ke aiwatarwa.

Sai dai Rufai ya dage cewa halin da miliyoyin ’yan Nijeriya ke ciki a yau ya saɓa da wannan fahimta, yana mai cewa tsadar rayuwa da ƙarin yawan mutanen da ke neman taimako shaida ce karara ta matsin tattalin arzikin da jama’a ke fuskanta.

Ya zargi mai magana da yawun shugaban ƙasar da rashin fahimtar hakikanin halin da talakawa ke ciki, yana mai cewa hauhawar farashin kayayyaki da raguwar ƙarfin saye sun ci gaba da jefa iyalai da dama cikin ƙunci.

Muhawarar ta sake tayar da kura kan halin tattalin arzikin Nijeriya, inda jami’an gwamnati ke cewa sauye-sauyen da ake aiwatarwa sun fara haifar da ɗa mai ido, yayin da masu sukar gwamnati ke cewa har yanzu miliyoyin ’yan Nijeriya na fama da tsadar rayuwa, hauhawar farashin kayan abinci da raguwar ƙarfin tattalin arziki.

A gefe guda, gwamnatin Shugaba Tinubu ta ci gaba da kare manufofinta na tattalin arziki, musamman cire tallafin man fetur da sauye-sauyen tsarin musayar kuɗaɗen ƙasashen waje, tana mai cewa waɗannan matakai sun zama dole domin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa, jawo hannun jari da kuma shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa a nan gaba.

By ukarofi

Leave a Reply