*An dakatar da Shugaban Kwamitin Amintattu
Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
Kwamitin Zartarwa na ƙasa na ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ya dakatar da Shugaban Kwamitin Amintattu na ƙungiyar, Alhaji Bashir M. Dalhatu, bisa zargin almundahanar kuɗi da take ƙa’idojin kundin tsarin mulki, a wani mataki mai tsauri da ya ƙara ruruta rikicin shugabanci a cikin ƙungiyar.
An yanke wannan hukunci ne a wani taron gaggawa na NEC da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, a daidai lokacin da ake taƙaddama kan rahotannin hana shiga hedikwatar ACF da ‘yan sanda suka yi gabanin tarurrukan da aka shirya gudanarwa.
Yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron, Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa, Farfesa Tukura Muhammad-Baba, ya ce wakilai daga jihohin Arewa kusan 18 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja sun samu damar halartar taron ne bayan da aka canja wurin taro daga hedikwatar ƙungiyar da aka rufe zuwa wani wuri a cikin Kaduna.
Ya bayyana cewa, NEC ta yi Allah-wadai da abin da ta kira hana shiga hedikwatar ƙungiyar ba bisa ƙa’ida ba, tana mai cewa hakan cin zarafi ne ga ’yancin haɗuwa da kuma harkokin cikin gida na ƙungiyar.
A cewarsa, NEC ta jaddada cewa babu cikakken rikici na shugabanci a ACF, sai dai rashin fahimtar tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma yunƙurin wasu mutane na mamaye ikon da bai dace da su ba.
Sai dai taron ya ɗauki sabon salo bayan nazarin rahoton Kwamitin ɗa’a da Ladabi da aka kafa domin binciken koke kan yadda ake tafiyar da kuɗaɗe da tsarin shugabanci a cikin ƙungiyar.
Farfesa Muhammad-Baba ya ce, binciken farko na kwamitin ya nuna akwai manyan batutuwan da ke buƙatar zurfafa bincike, musamman kan bin ƙa’idojin tafiyar da kuɗi da gudanar da mulki.
Bisa ga shawarwarin rahoton, NEC ta kada ƙuri’ar rashin yarda da Alhaji Bashir M. Dalhatu tare da amincewa da dakatar da shi nan take daga matsayin Shugaban Kwamitin Amintattu, har sai an kammala bincike.
Haka kuma NEC ta umarci a gudanar da cikakken binciken ƙwararru kan dukkan harkokin kuɗaɗen ACF, ciki har da Asusun Zuba Jari na ƙungiyar, tare da umarnin gano duk wani kuɗi da aka gano an tafiyar da shi ba bisa ƙa’ida ba.
Bugu da ƙari, NEC ta tabbatar da goyon bayanta ga Shugabancin Kwamitin Zartarwa na ƙasa ƙarƙashin Alhaji Mike Mamman Osuman, SAN, tare da tabbatar da matsayin Sakataren Janar har sai an yi duk wani gyara na kundin tsarin mulki.
ƙungiyar ta kuma yi Allah-wadai da matakin hana shiga hedikwatarta da aka danganta da ‘yan sanda, tana mai cewa hakan cin zarafi ne ga ‘yancinta na aiki da kuma ‘yancin tsarin mulkinta.
Wannan sabon mataki na nuna babban sauyi a rikicin cikin gida na ACF, yayin da saɓani kan shugabanci da ikon tafiyar da ƙungiya ke ƙara tsananta a tsakanin manyan ’ya’yanta.
