AFCON: Tinubu ya janye aniyyarsa ta zuwa kallon wasan Nijeriya na ƙarshe, ya wakilta Shettima a madadinsa

Spread the love

Daga BASHIR ISAH

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya janye niyyarsa ta zuwa kallon wasan karshe da Nijeriya za ta kara da Côte d’Ivoire a gasar AFCON 2023 da ke gudana a kasar Côte d’Ivoire.

 Maimakon haka, Tinubu ya wakilta Mataimakin Shugaban Kasa,  Kashim Shettima kan ya jagoranci tawagar Shugaban Kasa zuwa wajen kallon wasan wanda za a buga a ranar Lahadi.

Hadimin Shugaban Kasa kan sha’anin yada labarai da sadarwa, Stanley Nkwocha, shi ne ya  bayyana haka  a ranar Asabar.

MANHAJA ta rawaito da fari cewar, Tinubu zai halarci kallon wasan na karshe da Nijeriya za ta buga da Côte d’Ivoire domin karfafa wa ‘yan wasan gwiwa.

A cewar Nkwocha, “Gwamnatin Tarayya ta bukaci ’yan Nijeriya, wadanda ke gida da na ketare, da su hade kai wajen mara wa Super Eagles baya.”

Idan za a yi iya tuna, ko a wasan na kusa da na karshe da Nijeriya ta kece reni da Afirka ta Kudu, Shettima ya wakilci Tinubu wajen kallon wasan don karfafa wa ‘yan wasan gwiwa.

By Editor