An rantsar da Ademola Adeleke a matsayin sabon Gwamnan Osun

Daga BASHIR ISAH

An rantsar da Sanata Ademola Adeleke a matsayin sabon Gwamnan Jihar Osun a ranar Lahadi.

Da wannan, Adelek ya zama gwamna na shida aka zaɓa a jihar tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya ƙasar a 1999.

Alƙalin Alƙalan jihar, Mai Shari’a Oyebola Adepele-Ojo, shi ne ya jagoranci rantsar da Adeleke da misalin ƙarfe 11:45 na hantsi.

Bikin rantsarwar ya guda ne a babban filin wasannin motsa jiki da ke Osogbo, inda magoya bayan Jam’iyyar PDP da sauran baƙi daga ciki da wajen jihar suka haɗu don shaida rantsarwar.

A ranar 16 ga Yulin 2022 Adeleke ya lashe zaɓen gwamna da aka gudanar a jihar a ƙarƙashin Jam’iyyar PDP inda ya kayar da gwamna mai barin gado, Adegboyega Oyetola.

Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na PDP, Atiku Abubakar, na daga cikin manyan baƙin da suka halarci bikin.