Ana cece-kuce kan rufta Nijeriya yarjejeniyar auren jinsi

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Wasu malamai sun koka akan Gwamnatin Tarayya, domin sanya hannu akan yarjejeniyar

nan mai cece-kuce ta Samoa, wacce ake zargin ta na ƙunshe da amincewa da tsarin auren

jinsi.

A cewarsu, yarjejeniyar tana ɗauke da wasu sharaɗai da suka ƙunshi cewa ƙasashe masu

tasowa dole su yarda da ’yancin ’yan luwadi da ’yan maɗigo da kuma ’yancin yin auren jinsi

ɗaya.

Yarjejeniyar an samar da ita a tsibirin Samoa, inda aka sanya ma ta hannu a ranar 15 ga

Nuwamba, 2023, amma tun lokacin yarjejeniyar ke samun suka daga addinai da dama,

saboda hakan ya saɓa wa addininsu da al’adunsu.

Bayanai akan yarjejeniyar ya fito ne lokacin da Ministan Kasafin Kuɗi Da Tattalin Arziki, Alhaji

Abubakar Atiku Bagudu, ya bayyana irin halin da ake samu, a wata liyafa da Ƙungiyar

Ƙasashen Turai suka shirya a Abuja. Duk da dai ya ce, Nijeriya ta sa hannu ne a sashin bashin

Dala biliyan 150.

Ƙasashe da dama a duniya sun ƙi yarda sun sanya hannu kan yarjejeniyar a 2023 lokacin da

aka yi ta. Ƙasashen sun haɗa da Guinea, Trinidad and Tobago, Mauritania da wasu ƙasashen

Afirka da dama.

Yanzu haka wannan lamari ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta na Nijeriya, inda

’yan Nijeriya ke nuna allawadai da wannan lamarin.

Duk ƙoƙarin da Blueprint Manhaja ta yi na jin ta bakin Gwamnatin Tarayya kan lamarin, don

jin ƙarn bayani ya ci tura, domin Mai Magana da Fadar Shugaban Ƙasa, Abdul’aziz

Abdul’azil, bai amsa kiran da mu ka yi masa ba kuma har zuwa lokacin wallafa wannan

rahoton bai kira ba.

By ukarofi