Batun cire tallafin mai ya rikita ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Tun bayan da zaɓaɓɓen sabon Shugaban Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya furta kalaman cewa, an kawo ƙarshen biyan tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ke yi a ƙasar, al’amura suka soma rikicewa, inda kace-nace ya ɓalle kan batun, sannan kayayyaki suka yi mummunan tashin gwauron zabo, wanda ba a tava ganin irinsa ba a nan kusa, musamman ma farashin litar man fetur ya ninka kusan sau uku.

Shugaba Tinubu ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya ke gabatar da jawabinsa na farko a matsayin Shugaban Ƙasa ranar Litinin, 29 ga Mayu, 2023, inda cikin awanni da waɗancan kalamai sai aka fara ganin dogayen layika a gidajen mai.

Blueprint Manhaja ta yi nazari kan faruwar lamarin bisa la’akari da halin da ake ciki a faɗin ƙasar. Ga yadda rahoton ya nuna:

Farashin sufuri da kayan masarufi sun yi tashin gwauron zaɓi:

Cire tallafin man fetur da hauhawar farashin man fetir ya haifar da tashin gwauron zabi na sufuri da kuma farashin kayan abinci a faɗin Nijeriya.

A ranar Laraba ne Kamfanin Mai na Nijeriya (NNPCL) ya tabbatar da ƙarin farashin man fetur daga Naira 197 zuwa Naira 557 a wasu jihohi.

Blueprint Manhaja ta lura cewa wasu ‘yan kasuwa masu zaman kansu suna rarraba mai a kan Naira 700 kowace lita.

Babban Jami’in Sadarwa na Kamfanin NNPC, Garba Deen Muhammad, ya ce daidaita farashin ya yi daidai da “haqiqanin kasuwa”, inda ya ce kamfanin ya umurci kamfanonin da ke faɗin ƙasar nan su sayar da mai tsakanin Naira 480 zuwa Naira 570 kan kowace lita.

“NNPC Limited na son sanar da abokan cinikinmu masu girma cewa mun daidaita farashin famfo na man fetur a duk kasuwanninmu, daidai da gaskiyar kasuwa a halin yanzu.

“Yayin da muke ƙoƙarin samar muku da ingantaccen aiki wanda aka san mu da shi, yana da muhimmanci a lura cewa farashin zai ci gaba da canzawa dangane da yanayin kasuwa,” inji shi a cikin wata sanarwa.

Dangane da farashin da ake ta yaɗawa, an karɓi sabon jadawali na farashin dillalai don yankuna daban-daban na shiyyar ƙasar nan.

An umurci manajojin dillalan man fetur na NNPCL da su aiwatar da bitar daga ranar 31 ga watan Mayu duk da iƙirarin da aka yi na tanadin Naira tiriliyan 3.36 na biyan tallafin man fetur na watanni shida na farkon shekarar 2023 da gwamnatin da ta shuɗe ta yi.

Kamar yadda sabon jadawalin farashin man fetur ya nuna, za a sayar da man fetur a kan Naira 557 kan kowace lita a Maiduguri jihar Borno da kuma Damaturu a Yobe, yayin da a sauran jihohin Arewa maso Gabas za a sayar da shi kan Naira 550 kan kowace lita.

Birnin Kebbi za su sayi man fetur a kan Naira 545 a matsayin farashin da aka tsara a yankin Arewa maso Yamma. Matsakaicin farashi a shiyyar Arewa ta Tsakiya zai kai Naira 537 a kowace lita, sai dai a Ilorin, inda za a sayar da shi kan Naira 515 kan kowace lita. Masu amfani da su a yankin Kudu maso Gabas za su riƙa saye kan Naira 520 kan kowace lita.

Baya ga Uyo, Akwa Ibom da Yenagoa, Bayelsa inda a yanzu man fetur za a sayar da shi kan Naira 515, sauran yankin Kudu maso Kudu kuma za su samu kayan a kan Naira 511 kan kowace lita.

Lita guda Naira 500 a Kudu maso Yamma, amma Legas kan Naira 488:

Tuni dai gidajen man da suka haɗa da na NNPC da ke faɗin qasar nan suka daidaita farashin man fetur ɗin su yadda ya kamata.

‘Yan Nijeriya na kokawa yayin da ake yin dogon layi, da hauhawar farashin kayayyaki a jihohi

A ranar Laraba ne dai farashin sufuri a Abuja, Legas da sauran garuruwa ya ƙaru, sakamakon matsalar man fetur da ake fama da shi, lamarin da ya janyo dogayen layi a mafi yawan gidajen mai.

Tafiya daga Lugbe zuwa Sakatariya da Area 10 a Abuja wanda a da ana biyan N200, yanzu ya ƙaru zuwa N400 yayin da Nyanya/Mararaba zuwa Berger N400 daga N250/N300.

Daga Bwari zuwa Berger da Area 1 a yanzu N1,000/N1,200 daga N500, yayin da Kubwa zuwa Berger yanzu farashin N800/N1,000 daga N300.

Wani jami’in ƙungiyar ma’aikatan sufuri a ɗaya daga cikin manyan tashoshin motoci na Nyanya, ya ce kuɗin mota zuwa Kaduna da Kogi ya kai Naira 4,000 daga N3,500.

An ga matafiya a Legas suna tafiya mai nisa a sakamakon cillawar farashin sufuri tare da cunkoson ababen hawa wanda ya yi ƙamari sakamakon layukan da ake yi a mafi yawan gidajen man da ke jihar.

Oshodi zuwa Mile 2 wanda a baya N400 ya zama N800; Agbara zuwa Mile 2 yanzu ya zama N1,000 daga N500 yayin da matafiya daga Iyana-Iba zuwa Iyana-Ipaja ake sa ran za su biya N800 daga N300. Tafiya daga Costain zuwa Ikeja wanda ya kasance N400 yanzu N800 ne Costain zuwa Apapa wanda a da yake N200 ya koma N400.

A jihar Oyo an ƙara wa matafiya kuɗin mota. Tafiya daga Ojoo zuwa Total Garden ta tashi zuwa N500 daga N200; na Ibadan zuwa Legas, wanda a halin yanzu yana tsakanin N800 zuwa N1,200, an kai tsakanin N2,000 zuwa N3,500 a faɗin tashoshin mota daban-daban na jihar.

Manhaja ta kuma lura cewa an ƙara kuɗin jigilar fasinjoji zuwa Zariya daga Kano wanda daga Naira 1,500 zuwa Naira 2,000; Yayin da daga Zaria zuwa Kaduna yanzu ya zama N3,500 daga N2,000. Tafiyar Kano zuwa Abuja ta kai Naira 7,000 daga N5,500.

A Kano, wani mai aikin mota kasuwar Kantin Kwari, Suleiman Auwal ya ce, “Mun ƙara farashin ayyukan da muke yi a kowace tafiya daga Naira 500 zuwa Naira 1000 saboda muna amfani da man fetur wajen kai kaya ga abokan ciniki daban-daban.”

A Ibadan, kwanon garri da ake sayar da shi a kan Naira 350 ya zuwa ranar Litinin, yanzu ya koma N370 a babbar kasuwar Bodija. Haka abin ya shafi fulawa da aka ƙara daga N300 zuwa N350 a kowane kwano.

Tattaunawar ƙungiyar ƙwadago da Tinubu ba ta cimma matsaya ba:

Taron da Ƙungiyar Ƙwadago ta shirya da wakilan Gwamnatin Tarayya a fadar gwamnatin tarayya dake Abuja kan batun cire tallafin man fetur a ranar Laraba ya kare ne da zaman tankiya domin ba a cimma matsaya ba.

Ƙungiyar Ƙwadagon ta samu jagorancin Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya, Joe Ajaero da takwaransa na Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa Festus Osifo.

Waɗanda suka halarci zaman sun haɗa da tsohon gwamnan jihar Edo, Adams Oshiomhole; Babban Sakatare, Tijjani Umar; Shugabar Ma’aikata ta Tarayya, Folashade Yemi-Esan, Babban Jami’in Gudanarwar Rukunin, NNPC, Mele Kyari; darakta a rusasshiyar ƙungiyar yaqin neman zaɓen Tinubu/Shettima, Dele Alake, da sauransu.

Ajaero da Osifo sun shaida wa manema labarai bayan taron cewa matsayar ƙungiyar ƙwadago shi ne a ci gaba da kasancewa a kan farashin man fetur da aka sani, yayin da ake ci gaba da tattaunawa.

Sun ce za a sake yin wani taro bayan tattaunawa da wakilan shugabanninsu kan sakamakon ganawar da suka yi da tawagar gwamnati a ranar Laraba.

Ajaero ya ce, “Game da batun Ƙungiyar Ƙwadago, ba mu da wata matsaya a wannan taron.”

Ya caccaki matakin da Kamfanin NNPCPL ya ɗauka na sake duba farashin man fetur kafin taron, inda ya bayyana cewa ƙarin ya jefa ƙungiyoyin ƙwadago cikin tsaka mai wuya a yayin tattaunawar.

“Wannan ita ce qa’idar tattaunawa. Ba ku sanya abokin tarayya ba, kun tambaye su don yin shawarwari a ƙarƙashin manufar cire tallafin.

“Addu’ar ƙungiyar ta NLC ita ce mu koma kan matsayin da muke da shi, mu tattauna, mu yi tunanin hanyoyin da za mu bi da duk wani tasiri da yadda za a tafiyar da illar da wannan mataki zai yi wa jama’a. Idan aiki ne wanda dole ne a ɗauka.

“An yi tanadin tallafin har zuwa ƙarshen watan Yuni. Kuma kafin nan, mutane masu hankali, kula da ma’aikata, ya kamata gwamnati ta iya tunanin abin da zai faru a qarshen watan Yuni. Ba ka fara shi kafin lokacin b,” inji Ajaero.

Alake ya ce za a ci gaba da tattaunawa kan hanyoyin warware dukkan batutuwan da ke hannunsu.

Ya ce: “Mun daɗe muna tattaunawa kan samar da mafita mai gamsarwa game da batun da ke gaba, ga jadawalin da duk wannan da kuma ƙarin farashin famfo.

“Tabbas, Shugaban NNPCL yana nan, Mista Kyari, ba za mu iya yin cikakken bayani a yanzu ba saboda har yanzu tattaunawar tana ci gaba da gudana. Ba za mu iya kammala komai a wuri ɗaya ba, don haka, mun ɗage zaman yanzu, za mu ci gaba da tattaunawa nan gaba kaɗan.

“Amma batun shi ne tattaunawar tana ci gaba kuma yana da kyau kowane ɓangare su ci gaba da tattaunawa da nufin cimma matsaya mai gamsarwa wacce za ta kasance cikin dogon lokaci ga ‘yan Nijeriya. Wannan shi ne gwargwadon yadda za mu iya cewa yanzu.”

Wani masanin tattalin arziki, Dokta Bongo Adi, wanda babban malami ne a Kwalejin Kasuwanci ta Legas, ya ce cire tallafin man fetur ita ce hanyar da ta dace a bi domin hakan zai tabbatar da cewa masana’antar ta yi daidai da ƙa’idojin kasuwa.

Sai dai ya yi gargaɗin cewa kamata ya yi gwamnati ta yi jagora a kan lamarin da ‘yan kasuwa suka kafa wata ƙungiya don tantance farashin mai.