Mataimakin Shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima ya dawo Abuja bayan ziyarar kwana ɗaya da ya kai ƙasar Senegal, inda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a wajen bikin cika shekaru 65 da samun ‘yancin kan ƙasar.
A lokacin ziyarar tasa, Sanata Kashim Shatima ya halarci bukukuwan murnar samun ‘yancin kai na al’ada da aka gudanar, ciki har da wani faretin ban-girma da aka yi akan titin Mamadou Dia dake babban birnin ƙasar, ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bassirou Diomaye Faye.
Wakilan Najeriya a taron sun haɗar da
Ministan harkokin waje Ambassador Bianca Odumegwu Ojukwu da Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai Mai kula da Harkokin Waje, Hon Oluwole Oke.
